Yan bindiga sun sace daliban islamiya 8 da malaminsu a Katsina



Lamarin ya afku a Unguwar Sakkai karamar hukumar Faskari


A labarin da Katsina Daily Post News ke samu , na nuni da cewa wasu yan bindiga sun shiga kauyen Unguwar Sakkai dake cikin karamar hukumar Faskari, inda suka yi awon gaba da daliban wata makarantar islamiya a yayin da ake cikin dauka karatu.


Kamar yadda majiyarmu ta Katsina Post ta rawaito, lamarin ya afku ne a ranar Talata da yamma, daidai lokacin da daliban makarantar ke daukar darasi, inda suka kwashi dalibai 8 ciki har da malaminsu.


Sai dai da majiyar ta tuntubi Kakakin rundunar yan sandan jihar Katsina SP Gambo Isa, har kawo yanzun ba su kai ga samun ta bakinsa ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post